Document Body Page Navigation Panel
1
Ga Abubuwan Dake Ciki
Locaci Shafi
Kudancin Afrika na fuskantar matsalar cutar kanjamau 1min. 45secs 6
Kimanin mutane dubu 50 ke kamuwa da cutar kanjamau
a Afrika ta kudu kowani wata.
Afrika na fuskantar yunwa 1min. 37secs 3 Yake-yake, kamfar ruwa
da kwari suna sayawa abu
mawuyaci ga kasashen Afrika wajen ci da kansu
BUNKASAR ALKARI'U CIKIN HANZARI A AFRIKA
Alkari'un Afrika suna bunkasa cikin hanzarin fiye da sauran kasashen duniya
21secs 13
Afrika na samawa kanta kasuwa 2min. 45secs 7 Afrika na shirin jayo
hankalin masu zuba jari na duniya
Gibi Tsakanin Maza da mata kan ilmi a makarantun
Afrika 46secs 13 Yaran maza ke shiga makarntu fiye da mata a yawancin
kasashen Afrika
Sabon Maganin kare jarirai daga cutar kanjamau 1min. 32secs 6 Sabon
maganin da aka samu a Uganda da Amurka na
bada kwarin gwiwa ga 'yan baya masu zuwa
Azabtar da yara ya zama ruwan dare a Uganda 2min. 3secs 10 Yara
a kasar Uganda suna fusukantar bakar azaba
daga iyayen su
Mata da yawa ke zaman jarun a kasar Sudan 1min. 53secs 5 Cinikin
barasa ya jefa matan kudancin Sudan
dubbai gidan jarun a kowace shekara
Bacewar halittu a Duniya 2min. 45secs 7 'Yan baya masu zuwa bazasu
gafarta mana ba
saboda halakar da wasu halittu da jama'ar yanzu keyi.
Za'a gabatar da wani shirin kare kogunan turai 1min 11secs 5 Hukumar
WWF ta shirya kaddamar da yekuwar kare
kogunan kasashen turai. 1
1 Page 2 3
Vol 11 No 10
September 1999 (Hausa) CHANGE Radio
2
Kasar Canada na da muhimmanci kan gandun dazuzzuka a duniya 26secs 14
Kimanin kashi goma cikin dari na gandun dajin
duniya na kasar Canada
Matsalar karancin ingantacen ruwa 14secs 13 Kusan kowani mutun guda
daga cikin mutane uku
a duniya zai fuskanci matsalar karancin ruwa nan
da shekaru 50
Shinkafaa mai yawa da ruwa kalilan 2min. 34secs 8 Rashin isashen
ruwan sama a duniya na jefa noman
shinkafa cikin mawuyaci hali, masana kimiya na
samo sabbin dabarun noma da ruwa kalilan.
Zanzibar ta haramta shigo da kifin tabki 1min. 50secs 4 Zargin yin
amfani da guba ya sanya an haramta shigo da
danyen kifi da ake kamawa daga Tabkin Victoria a
gabshin Afrika.
Najeriya ta kafa sabbin Gandun Dazuzuka 51secs 3 Wasu gandu dazuzzuka
biyu an maida su na kasa
Italiya na daukar Tsauraran matakai kan masu cinnawa dazuzzuka wuta 44secs
13
Italiya ta kuduri aniyar dakatar da masu cinnawa
gandun dazuzzuka wuta
Tauraron dan adan zai iya gano alamar barkewar annobar zazzabi 2min.
7secs 9
Bayanin tauraron dan adan zai taimaka wajen kare
mummunar annobar dabbobi.
Tsuntsayen dake sanin lokaci 59secs 14 Masana sun gano abin mamaki
a kasar Indonesia
Zaki da bera 10 Aikata alheri
Meyasa jemagu ke tashi da dare? 1min. 5secs 11 Jemagu suna gani
da dare
Mumunar laifi da kadima kurege ya aikata 4min. 10secs 11 Gano
dalinlin da yasa damisa ke farauta ita kadai 2
2 Page 3 4
Vol. 11 No 10
September 1999 (Hausa) CHANGE Radio
3
Labaru
Afirika na fuskanta yunwa 1min. 37secs
Sama da mutane miliyan goma daga kasashen Afrika goma sha-6 ne ke bukatar
taimakon gaggawa na kayan
abinci domin kaucewa yunwa. Wanan kuwa na kunshe ne cikin bayanin da hukumar
kula da abinci da aikin
gona ta duniya dake birnin Roama ta bayar.
Yakin basasa, kamfar ruwa da kwari, sune suka gurgunta aiyukan samar da abinci
a sashin Sahara na Afrika,
inda dubban daruruwan mutane ke fuskantar barazanar yinwa inji hukumar a ranar
16 ga watan Agusta.
Ance kasar Angola ce barazanar tafi muni, inji jami'in hukumar ta abinci Mrs.
Mwita Rukandema, wadda tace
kazancewar yaki kwanan nan tsakanin dakarun Gwamnatin Angola dana 'yan twayen
kungiyar UNITA, ya
sanya baby damar kai duk wani taimakon kayan abinci ga jama'ar da suka gudu
suka bar gidajen su a sandiyar
fadan.
Dakarun na UNITA, wadanda aka bada rahoton cewar su nayiwa motoci kwanton
bauna tare da harba
mayan makamai a manyan garuruwan kasar.
Jami'ar Rukandeman tace in har wannan hali ya cigaba man da watani biyu, za
a ji mugun labari game da
matsananciyar yunwa.
Rukandema tace hanya guda da za'abi domin kaucewa wannan bala'i, itace ta
matsawa dakarun Gwamnati
dana 'yan tawayen lamba, domin kyale yin amfani da jiragen sama, sauka a wasu
filayen jiragen same 'yan
kalilan wajen kai kayan abinci da magunguna.
Dayawa daga cikin 'yan kasar ta Angola da baki 'yan kasashen waje da sukayi
kokarin kai kayan abinci, 'yan
twayen su kashe su.
Africa News On Line.
Nageria ta kafa sabbin gandun dazuzuka 51secs
Ranar 3 ga watan Agusta Gwamnanti Najeriya ta kaddamar da gandun dajin Okomu
dake kudancin kasar da
gandun dajin Kamuku dake arewacin kasar a matsayin gandun dazuzuka na kasa.
3
3 Page 4 5
Vol 11 No 10
September 1999 (Hausa) CHANGE Radio
4
An kafa gandun dajin Okomu nee shekaru goma sha-5 da suka wuce dake gandun dajin
a matsayin na gwaji,
wanda hukumar kula da dazuzuka na Najeriya, wanda ke karkashin hukumar kare
dabbobi da halittu ta duniya
(WWF). Gandun dajin dake da fadin kilomota dari da goma sha-2 murabba'I, wuri
ne dake da dausayi da
tsuntsaye iri-iri dakuma namun daji iri-iri ciki har da giwaye dakuma birra
masu farin wuya.
Wanan kuwa gagarumin ci gaba ne da aka samu inji darektan kula da gandun dazuzika
na kasa, Alhaji Lawan
Marguba.
Paddy Ezeala/ WWF
Zanzibar ta haramta su a tabki 1min 50 secs
Kasar Zanzibar ta harmta shigo da kifin da aka kama daga Tabkin Victoria,
watanni biyu bayan kungiyar
kasashen Turai ita ma ta haramta shigo da irin wadan nan kifin daga yankin,
a sakamakon rahotanin da aka
bayar na cewar masintan yankin na amfani da guba wajen kamun kifin.
Cikin sanarwar da Ministan gona da, raya dabbobi da albarkatun kasa, tace
anyi haka ne domin kare masu cin
kifin ciki harda masu zuwa yawon bude ido dakuma tattalin arzikin tsibirin.
Burgediya-Janar Adam Nwakanjuki yace koda shike babu tabbas kan ko tabkin
na Victoria ya gurbace da
guba, kasar Zanzibar ba zata yi kasadar kasancewa wurin da za a rika jigbe kayan
abincin da suka lalace ba.
Haramcin wanda ya hada da kifin da aka samu daga kogin Nilu ya biyo bayan
yadda ake kara samun irin
wadan nan gurbatatun kifayen daga kogin na Nilu. Yanzu haka Gwamnati ta sanya
jamian da zasu rika sa ido
a tasoshin jiragen ruwa dake tsibirin dakuma tasoshin jiragen sama da Otel-Otel
dakuma manyan kantunan
ciniki irin na zamani, danufin hana shigo da kifayen da ake samu daga tabkin
na Votoria da kuma kogin na Nilu.
Wani babban jami'in hukumar kula da yawon bude ido na Zanzibar yace duk Otel
din da aka samu yan amfani
da wadan nan kifin, za a soke lasisin sa. A makon jiya ne Gwamnatin Tsibirin
ta umurci dukkan otel-otel din da
suke da kifayen na kogin Nilu da su lalatasu.
Haramta sigo da kifaye daga Gudarin kasar Tanzania da Kenya dakuma Uganda
yazo ne makwani uku kacal
bayan da Zanzibar ta haramta saida wani irin ruwan kwalba da ake kira MASAFI,
wanda akeyin sa a Dar es
Salam. Gwamnati Tsibirin tayi ikirarin cewar kwajin da aka gudanar daga jamin'an
kula da harhada magunguna
an gano cewar ruwan bai dace jama'a su sha ba.
Africa News On Line 4
4 Page 5 6
Vol. 11 No 10
September 1999 (Hausa) CHANGE Radio
5
Shirin kare kogunana turai 1min 11secs
Za afara wani gagarunin shirin kare kogunan kakashen Turai daga wannan watan
na Satumbar 1999. Shirin
wanda akayiwa taken 'Rayayyun Koguna' zai kunshi dukkan nhiyar, wada hukumar
kare halittu da dabbobi ta
duniya WWF zata aiwatar. An tsara shirin ne ta yadda za a wayarwa da jama'a
kai su san muhimmanci da
aiyukan koguna tare da nuna irin barazanar da suke fuskanta saboda rashin kulawa
tare kuma da irin rawar da
jama'a da kungiyoyi zasu taka wajen kula da ruwa.
Kamar yadda hukumar ta WWF ta fadi shirin yekuwar zai samarwa da kogunan na
Turai da tsarin kula tare da
manufofi na kwarai.
Za'a kaddamar yekuwar ne a Brussel ranar 21 ga watan Satumba, a halin yanzu
kuma za a kaddamar da wani
littafi mai warka 20 a karshen watan Agusta, wanda ke da taken RAYA KOGUNAN
TURAI. Tsarin sha
yanzu magani yanzu. Shirin na sha yanzu magani yanzu, zai kalubalanci kungiyar
kasashen Turai, Gwanmatocin
kasashen da kananan hukumoni masana 'antu da 'yan kasuwa, masu samar da ruwa
da sauran kungiyoyin da
ke da sha'awa a wannan fanin, domin daura damara wajen daukar matakan da suka
dace, inji hukumar ta
WWF.
WWF
Mata da yawa ke zaman jarun a kasar Sudan 1min 53secs
Sama da mata dubu talatin ne suke zaman jaron na wa 'adi dabab-daban a Sahin
Arewacin kasar Sudan inda
Musulmi ke da rinjaye, akasarin su saboda aikata kananan laifuffuka.
Wannan kuwa yafi kashi daya cikin dari na yawan al'umar kasar. Kashi casa'in
da biyar cikin dari na wadan
nan matan a daure su ne saboda laifin girka barasa dakuma sayarwa, kuma kusan
dukkan su sun fito ne daga
sashin kudancin kasar ta Sudan inda ba laifi bane girkawa ko saida barasa dakuma
dirkan sa.
Kamar yadda rahotanin baya-bayan nan ya nuna fiye da rabin adadin Matan an
sake kama su ne bayan da aka
sako su. Kayan da ake girka barasan kuwa wasu matane fittatu ne ke sayar dasu
da arba ta hanyar gwanjo inji
rahotannin. Matan su kan baron gidan kason ne su je su sayi kayan girka barasan
kana su cigaba da sana'ar
ta su da suka saba.
Akasarin matan dai masu juna biyu ne ko kuwa suna shayar da jarirai. Fiye
da yara dari a ke haihuwar su a
kowace shekara a daya daga cikin gidajen jarun din, yayinda wani gidan akan
haifi kimanin yara dari biyu
yayinda iyayen nasu ke zaman kaso. 5
5 Page 6 7
Vol 11 No 10
September 1999 (Hausa) CHANGE Radio
6
Koda shike ance gidajen Jarun na Sudan na daya daga cikin mafiya kyau a Afrika,
tuni ake da kira domin sake
tsarin gidajen ta yadda za arika kula da matan da suke fama da tasku a sashin
Arewacin kasar saboda al'adar
su ta saida barasa.
Newslink Africa
Sabon maganin kare jariban da iyayen su ke
fama da cutar kanjamau 1min 32secs
An samo wani sabon maganin da zai iya kare jariran da iyayen su ke dauke
da cutar kanjamau, kamar yadda
binciken da wasu masana daga kasashen Amruka da Uganda suka gudanar a Kampala
da Washington.
Sakamakon farko da aka bayar baya aiyukan bincike na shekaru biyu ya nuna
cewar maganin zai kare jaririn
da uwar sa ke dauke da kwayoyin cutar HIV, wanda ke kaiwa ga cutar kanjamau,
in har anywa uwa wannan
maganin yayinda take haihuwa dakuma shi jarinrin bayan yayi kwana uku da haijuwa.
Ana cin karfin cutar da kimanin rabin karfin ta ta hanyar amfani da wannan
sabon maganin, idan aka kwantata
da maganin AZT-, wanda ke da tsada ninki 70, kamar yadda ma'aikatar lafiya ta
Amurka tayi bayani. Wanan
bincike shine mafi muhimmanci da ingaci yazuwa yanzu kan kokarin da akeyi na
kare yaduwar wannan muguyar
cutar ta kanjamau tsakanin iyaye mata da jariran su a duniya inji Dr. Anthony
S. Fauci na tsangayar kula da
cututtuka masu yaduwa, wanda ta dauki nauyin tafiyar da binciken.
Haka kuma wannan sakamakon ya samu gagarumin marhabin a Kampala. Wannan bincike
ya bada kwarin
gwiwar cewar akwai alamun kare jama'ar kasashen Afrika masu zuwa nan gaba daga
kamuwa da ita wannan
cutar ta kajamau, inji Ministan kula da aiykan lafiya na Uganda Cripus Kiyonga.
Newslink africa
Sharhi
Kudacin Afrika na fuskantar matsalar cutar kanjamau 1min 45secs
Cutar kanjamau ta fara faskara a kudancin Afrika duk da kokarin da Gwamnatoci
da kungiyoyi masu zaman
kansu da sauran al'umomi keyi na wayarwa da jama'a kai game da matsalar cutar.
Daga kididdigar da aka gudanar ta nuna cewar kasashen Botsuwan, da Namibia
da Swizaland dakuma Zimbabwe
sune cutar tafi muni a kudancin na Afrika. Kusan rubuin al'umar kasashen duk
sunharbu da kwayoyin cutar ta
HIV ko kuwa cutar kanjamau din baki daya. Kusan rubu'in wadanda suka kamun,
mutane ne da shekarun su
ya kama daga goma sha-5 zuwa arba'in da tara. 6
6 Page 7 8
Vol. 11 No 10
September 1999 (Hausa) CHANGE Radio
7
Kamar yadda Mujallar TIME ta Amurka ta wallafa ma'aikatar lafiya ta Afrika ta
Kudu tayi kiyansin cewa,
akalla kashi 20 cinkin dari na yawan ma'aikatan kasar ne zasu kamu da kwayoyin
cutar yazuwa badi. Cinkin
shekaru uku man gaba kuma kimanin mutane dubu metan da hamsin ne za su rika
mutuwa a duk shekara a
sansadiyar cutar wadda zata bar muatane dubu dari shida marayu. Haka kuma cutar
zata rage yawan shkarun
da ake saran mutane za suyi da shekaru ashirin hakan zai sanya tattalin arzikin
kasar ya rago da kashi biyu cikin
dari.
Cutar zatayi matukar illa ga tattalin arziki, muddin ba a bullo da kwararan
matakai da shirye-shirye ba wadanda
zasu kyautata harkokin kwadago da ingantuwar aiki, kamar yadda rahoton hukumar
raya kasa ta duniya
UNDP ta bayar.
Ministan lafiya na Afrika ta kudu Nkosazan Zuma yace mutanen kasar suna kamuwa
da kwayoyin HIV cikin
hanzari, wanda a duk wata kimanin mutane dubu hamsin ne ke kamuwa da cutar.
Wanan kuwa baban hatsari
ne ga kasar. Hakan ya nuna akwai gyara bisa damarar da kasar tayi na yaki da
yaduwar cutar ta kanjamau.
Newslink Africa
Afrika na samun karbuwa kan kasuwanci 2min 45secs
Ganin demukuradiya ta kankama a Afrika, mayan kasashen duniya sai nuna sha'awa
sukeyi game da zuba jari
a nahiyar. Cikin watan Oktoba, za'ayi taron kwanaki biyu a Dakar ta kasar Senegal,
inda manyan kasashen
duniya da kungiyoyin raya kasa zasu hallara domin tattaunawa. Daga cikin wadanda
zasu hallara su hada da
Ministoci daga kasashen Turai da manyan kamfaonin 'yan kasuwa da sugabanin Afrika
da Minintocin su na
kudi. Kamar yadda mjallar Newslink Afrika ta ruwaito baki daga kasashen Turai
sun hada da Ms. Clare Short
Sakatariyar kula da raya kasashe na Biritaniya, da Mr. Paul Neilson Ministan
raya kasashe na Denmak.
Sauran sun hada da Mr. Kenzo Oshima babban darektan tattalin arziki da raya
kasashe dake Japan da Ms.
Hilde F. Johnson Ministar raya kasa da kasa da kare hakkin dan adam na Norway.
Haka kuma Ms. Evelyn Kerfkens Ministar raya kasashe ta Netherlands da manyan
jami'an kasashen Faransa
da Jamus da Finland dakuma Italiya duk zasu halarci taron. Taron na hadin gwiwa
ne tsakanin kungiyar raya
masan'antu la duniya UNIDO, da kungiyar habaka masan'antu ta Afrika (AAI) da
hukumar raya tattalin
Arzikin Afrika (ECA) da Bankin raya Afrika (ADB) dakuma kungiyar hada kan kasashen
Afrika (OAU).
Daga cikin batutuwan da za a tattauna a taron su hada da tsarin bunkasa masana'antu
a Afrika da yanayin
harkokin zuba jari a haniyar dakuma hadin ka yankuna da kawancen kungiyar Tuari
da Afika da sha'anin
samar da kudaden kafa kananan masana'antu. 7
7 Page 8 9
Vol 11 No 10
September 1999 (Hausa) CHANGE Radio
8
Taron na Oktoba ya biyo bayan yekuwar Harare ne da akayi a shekarar 1997. Yekuwar
ta sanya babban
sakataren kungiyar OAU tare da hukumar raya kasa UNIDO da babban sakataren hukumar
ECA kan su
shirya taro da manyan kasashen dake bada taimako na duniya ta yadda za a samo
hanyoyin samar da kudaden
aiwatar da aiyukan raya kasa na sha yanzu magani yanzu.
Masu shirya taron suna fatar taron zai gaggauta habaka masana'antu a Afrika
ta hanya baiwa kasashen Afrika
damar samun sabbin abokan huldar kasauwanci ciki da wajen nahiyar ta Afrika.
Hadin kai ta fuskar fusaha shine babban jigo wajen kyautata yanayi domin zuba
jari a kasashen da dama.
Haka kuma zai kara kyautata samar da masana'antu masu karfi na 'yan kasa, wadanda
zasu tafi tare da
manyan masu zuba hannayen jari na kasashen duniya, inji rahoton da Newslink
Afrika.
Newslink Africa
Shinkafa mai yawa da ruwa kalilan 2mins 34secs
Kokarin gaggawa da akeyi na samar da wata dabarar noman shinkafa tare da
ruwa kadan kwalliya ta fara
biyan kudin sabulu. Domin kuwa an samo wata dabarar noman shinkafa mai yawa
da ruwa kalilan. Kungiyar
binciken aikin gona da bayar da shawarin kwaruru ta duniya CGIAR ce ta bullo
da dabarar samar da dausayi
da ingantacen iri, da kyautata filayo domin noman shinkafar.
Ita wannan sabuwar dabarar ta rage yawan muhimmancin samar da ruwa, domin
samun amfani mai yawa kan
kowace dadadar gona. Saidai kuma kungiyar ta CGIAR bata bada dalla-dallar bayani
kan yadda sabuwar
dabarar zatayi aiki ba. Duk da haka shugaban kungiyar Isma'il Seragendin kuma
mataimakin shugaban Bankin
Duniyan kan aiyuka na musamman yace shinkafa tana bukatar ruwa ninki biyu fiye
da kowace tsaba kana
sama da tan dubu biyu na ruwa ake amfam\ ni dashi domin noma tan guda na shinkafa.
Wanan yanayi kuwa zai
kasance mawuyaci ganin yadda ake samun koma baya kan samar da ruwa tare da yawan
bukatar samun
shinkafa a duniya.
Fiye da rabin mutanen duniya zasu dogara ne kan shinkafa, nan da shekaru 30
masu zuwa. Yankunan da ake
noma shinkafa a sashin Arewachi da Kudancin Najeriya suna fuskantar baranzanar
giggina madatsun ruwa,
dakuma bukasar alkari'u watakila sabuwar dabarar ta farfado da nomar shinkafa
sannu kan hankali. Ganin
yadda ake asarar filayen noma cikin hanzari, domin bunkasar garuruwa da lalacewar
dausayin kasar noma
matsalar ta zama babba da ake fuskanta inji babban Darktan kungiyar ta CGIAR
Ronald Cantrell dake da
cibiya a kasar Filifin. 8
8 Page 9 10
Vol. 11 No 10
September 1999 (Hausa) CHANGE Radio
9
Sabuwar dabarar tana iya taimakawa wajen kyautata tattalin arzikin kasashe masu
tosowa na duniya. Akasarin
kasashen dake nomar shinkafa kasashe ne masu tasowa wadanda Bankin duniya yace
samun su dan kalilan
ne. Nahiyar Asia na da kasashe goma sha-7 daga cikin kasashe 25 manya dake noma
shinkafa. Suna nome
fili mai fadin kashi case'in daga cikin dari na yawan filayen da ake noma shinkafa
a duniya suna samar da kashi
casa'in cikin dari na shinkafar da ake nomawa a duniya. A hakikan gaskiya ma
kashi daya cikin uku na
kasashen Asia dake noma shinkafa ce suke nomawa a ciki.
CGIAR
Hango barkewar zazzabi mai Tsanani ta hanyar tauraron-dan adam 2mins 7secs
Ana iya kare aukuwar barkewar kwayoyin cutar nan dake haddasa cutar dake
kashe garkunan shanu masu
yawa a gabshin Afrika, wanda kuma ke janyowa jama'a shiga halin tasku. Daga
binciken da aka gudanar ya
nuna cewar cutar tana da sahihiyar hanyar da take sake zagayowa. Ana iya hango
sake zagayowar cutar
watani hudu kain aukuwar ta, ta hanyar yin amfani da tauraron dan adam dakuma
daukar matakan lalata
kwayoyin cutar.
Masu binciken su gano cewar zagayowar cutar a ko yaushe yanayin kicibis da
daminar da aka samu ruwan
sama mai yawa a yankunan masu yawa na gabashin Afrika. Sunyi nazain yanayi na
shekaru hamsin, sun gano
cewar, cutar ta bulla shekaru goma sha-7 da suka wuce, wanda kuma yayi kicibis
da daminar da aka samu
ruwan sama mai yawa. Daga bisani kwayoyin cutar sukan bace tsakanin bullowar
ta.
Wanan kuwa cibiyar binciken kimiyar Amurka NASA da ma'aikatar kare kwayoyin
cuta ta duniya dake
cibiyar bincike ta Walter a Washington DC ne suka gano.
Kamar yadda bincike ya nuna, Sauro Aedes dake yada kwayoyin cutar, suna sanya
kwayoyin ne a kwayayen
su, wanda duma ke yaduwa a wuraten dake da dausayi bayan da aka samu ambaliyar
ruwa. Su kuwa
kananan Sauron suna samun abincin su ne a jinkin dabbobi. Haka abin zaiyi yaduwa
ba tare da la'akari ba har
sai sun yadu sosai. Dabbobin da suka ci wadan nan kwayayen Sauron su zasu kamu
da cutar, wanda daga
bisa in mutane sunci naman dabbobin sai su rika kamuwa da cutar zazzabin mai
tsanan. Shi kuwa irin wannan
Sauron yana yaduwa ne a locacin da aka samu damuna mai ruwa sama sosai.
Masu binciken suce wannan tauraron dan adam zai taimaka wajen hango ko hasashen
barkewar annobar
cutar watani shida kafin aukuwar sa. Abin sha'awar anan shine tauraron dan adam
din, zai iya yin gargadi tun
kafin barkewar annobar, kana ya gano ainihin yankunan da abin zai faru, inji
wani kwararen masanin halittu
Compton Tucker, wanda yayi amfani da tauraron dan adam, wajen yin nazarin halittu
a Afrika na tsawon
shekaru 20.
Environmental News Network 9
9 Page 10 11
Vol 11 No 10
September 1999 (Hausa) CHANGE Radio
10
Azabtar da yara ya zama ruwan dare a Uganda 2min 3secs
Iyaye suna yawan dukan 'ya 'yan su tare da yi musu fyade ba kuma tare da
an dauki matakan shawo kan
lamarin ba. Wannan kuwa na kunshe ne cikin rahotton da jaridar Monitor da ake
bugawa rana-rana a Uganda
ta 13 ga watan Yuli.
Jaridar ta ruwaito cewar wani locain anayiwa yara dukan kawo wuka a gidaje
da makarantu. Wasu ma har
kashe su akeyi ta hanyar azabtarwa daga su iyayen saboda 'yan laifukan da basu
taka kara su karya ba, irin su
samartakar Bera ko rashin kawowa uban su agogo cikin lokaci yayinda yake kokarin
zuwa aiki. Hanyar da
akafi azabtar da yara, itace da daure hannun su da igiya, kana a rufe da ganyen
ayaba ko takarda, kana a sanya
a kan wuta inji jaridar. Haka kuma jaridar ta Minitor tayi tir kan yadda akeyiwa
yaran mata kanana fyade,
wasu kan dududu ba su wuce shekaru uku da haihuwa ba.
Kwanan nan ne Gwamnatin Uganda ta daga yawan shekarun yiwa 'yan mata aure
daga goma sha-4 zuwa
goma sha-8, domin kare su. 'Yan kasar Uganda da abin ya dama suna kura da babbar
murya kan Gwamnati
ta kara yin kuduri wajen kare yara mata. Babbar mataalar azabtar da yara, shine
Gwamnati ba ta dauki batun
da muhimmanci ba inji jaridar ta Minitor, cikin sharshi ta. Baya ga kungiyoyi
masu zaman kansu, Gwamnati
bata kashe kudi wajen gudanar da bincike, ko shirya taruruka na kasa ta yadda
za a karfafa gwiwar shawo kan
wannan matsala ta azabtar da yara.
Africa News On Line
Zaki da bera
Zaki wanda ake dauka a matsayin sarkin dawa, saboda karfin da yake dashi
yana kuma ladabtar da duk wata
dabbar da ta nemi wuce makadi da rawa. Domin haka dukkan mamun dawa suna tsoron
sa kuma suna masu
biyayya gare shi, bugu da kari kuma suna bakin kakarin su na kaucewa duk wani
abu da zai bata masa rai.
Dukkan dabbobi suna kokarin ganin dangantakar su da sarkin dawa Zaki ta kara
kyautatatuwa.
Wata rana Zaki na barci, sai Bera cikin rashin sani ya taka bancin sa. Yayinda
zaki ya tashi cikin fushi, sai ya
kama bera yana son ya kashe shi, shine bera ya roki sarkin dawa da yayi masa
rai. Yace watakila wata rana
shima zai taimakawa zaki. Shine zaki yayi mamaki, har abin ya bashi dariya,
ganin bera dan tsurut dashi har
yace zai iya taimakawa zaki, wanda shine sarkin dawan dabbobi. Duk da haka dai
sai ya sake shi amma fa sai
da ya ja kunnen sa kan kada ya kuskura ya sake tadashi daga barci. Bera yayi
godiya kana ya tafi gida. 10
10 Page 11 12
Vol. 11 No 10
September 1999 (Hausa) CHANGE Radio
11
Baia dade ba da yin haka, ran nan sai zaki na yawo cikin daji, sai ya fada cikin
tarkon da maharba suka kafa.
Yayinda zaki yayi ta ruri, domin neman dauki, dukkan sauran dabbobin sai sukayi
biris dashi, tunda yake suna
tsoro in har sun sako shi yana iya halaki su. Daga karshe dai sai bera yaji
kukan zaki, sai ya tuna da irin alhinin
da zaki yayi masa yayinda ya taka hancin sa yana barci, domin haka sai ya kuduri
aniyar zuwa ya taimaka
masa.
Yayinda ya doso zaki sai ya ga ashe taron na kirtani ne. Sai bera ya fara
daddatse kirtanin da hakoran sa kan
ajima sai gashi yayi katuwar kofa ta yadda zaki zai iya fita. Yayinda bera ya
ceci zakin sai yace dashi, yayinda
ka ceci rai na nace dakai nima watalila wata rana zan cece ka, sai kayi dariya,
kace sarkin dawa da kanka yaya
ni bera zan iya taimaka maka.
Domin haka dai aikata alheri ga kowa, ba asan gobe ba.
Character moulding Stories for Better Citizenship.
Meyasa Jamagu ke tashi da dare 1min 5secs.
Jamagu kamar sauran dabbobi basu da wata hanyar kare kansu. Domin haka dahun
dare shine makarin su.
Babban abokin gabar su shine Duji, wanda ke yawo da dare domin neman abinci
yayinda suma jemagu ke
barin wuraren zaman su irin su kogo ko kuwa bishiyoyi. Wasu daga cikin jemagun
suna cin kwari, yayinda ba
mai ganin su. Saboda haka jemagu suna yawo ne cikin dare saboda kare kan su,
dakuma samun abincin su
cikin sauki.
Daga cikin dukkan dabbobin duniya jemage ne dadai ke tashi kamar tsuntsu.
Fukafukin su fata ce da ta lullube
yatsun su dakuma dogayen kafafun su har baya. Wasu mutanen suna daukar cewar
jemagu basa gani. Kokadan
ba gaskiya bane Domin kuwa jemagu suna da idanu dana suna gani saari cikin dare.
Chongololo
Mummunan laifin da Kurege Kadima ya aikata 4mins 10secs
Wata kabila da ke kira Hambakush dake kudancin Afrika, sun bada labarin
wani kureje da wata damisa da
'ya 'yan ta. Sun kulla yarjejeniyar cewa, kureje zai rika kula da 'yan 'yan
damisar yayinda ta tafi neman abinci,
ita kuwa damisar zata rika baiwa kureje abinda ta samo daga wajen farautar ta.
Sunan kureje Kadima ita
kuwa damisa suna ta Nthoo.
Ita wannan yarjejeniyar tayi ta aiki tsakanin su, har yazuwa locain da aka
samu kamfar ruwa a kasar. Namun
dajin da ita Nthoo take farautowa duk su gudu zuwa yankunan dake da ruwa, domin
haka damisar ta fara
fuskantar mawuyacin hali na rashin abinci tare da Kadema dakuma 'ya 'yan ta.
Kwanan da kawanki Nthoo
yadda ta tafi haka take dawowa hannun ta rabbana babu abinci. Nan da nan yunwa
ta fara addabar su. 11
11 Page 12 13
Vol 11 No 10
September 1999 (Hausa) CHANGE Radio
12
Wata rana Ntooo ta komo daga wajen faruta sai ta samu Kadima na cin nama, shine
sai ta tambayeshi ko ina
ya samu abinci, yayinda itama da ta shiga daji domin neman abin kalce bata samu
ba. Sai Kadima ye kada
baki yace, wata 'yar karamar dabba ce tazo wucewa bakin kogo, shine na kokarta
na kashe. Amma gaskiyar
lamarin shine naman da Kadima ke ci naman daya daga cikin 'ya 'yan damisar ne.
Washe gari Nthoo ta fita faruta, sai Kadima ya sake kashe daya daga cikin
'ya 'ya ta biyu da suka rage ya
cinye. Yayinda damisar ta komo da marice hannun ta rabbana Kurege sarkin wayo,
sai ya dauko mata dan
nata guda da ya rage, bayan ta bashi nono sai ya shigar dashi ya sake fitowa
dashi yace ga na biyu, bayan ta
bashi nono sai ya shigar dashi ya sake fitowa dashi yace ga na biyu, bayan ta
bashi nono ya sake komawo
dashi ya fito dashi yace ga na ukun su.
Washegari bayan da Nthoo ta fita faruta, sai kurege kadima ya sake kashe ragowara
dan nata ya lakwame.
Domin kare laifin da ya aikata, sai ya karkarya rassan itatuwa yayi ta birgima
a laka, yakuma shafa jar kasa a
jikin sa kamar jini, yayi kamar anyi gumurzun fada.
Yayinda Nthoo ta komo gida, sai kurege yazo gare ta yana tafiya kata-kata
yana kuka ya shaida mata cewar,
wasu mutane ne suka zo suka kashe 'ya 'yan ta suka tafi dasu cikin kauye domin
su cinye su. Yace yayi kokari
domin kare 'ya 'yan amma maharbar suka nada masa dan karen duka, har ma sun
kusa kashe shi. Shine ya
nuna jar kasar da ya shafa a jikinn sa da cewa jinin dukan san ne.
Nan take Nthoo damisa tayi wani kugu cikin daren wanda ya girgiza jama'a.
Cikin fushi ta nufi kauyen dake
kusa dasu, domin daukar fansa kan mutanen da suka kashe 'ya 'yan ta. Yayinda
damisa ke kokarin auka wa
wasu yara sai taji wani tsuntsu yace Kadima ne ya kashe miki ya ya.
Sai Nthoo ta juya da baya a fusace domin aukawa Kadima kurege, amma yayinda
Kadima yaji tautasuwar nan
tana fadawa Nthoo sai yace kafa me naci ban baki ba. Nthoo damisa bata samu
ta kama Kadima kurege ba,
amma mutanenen Hambakush suce har yanzu Nthoo tana cigaba da neman Kadima. Shine
yasa har yanzu
damisa take kaffa-kaffa kana take farauta ita kadai. Kuma shi yasa kurege yake
gudu a kodayaushe domin
tsirar da ransa batare da yana waiwaye ba.
When Hippo Was Hairy 12
12 Page 13 14
Vol. 11 No 10
September 1999 (Hausa) CHANGE Radio
13
Gibi Tsankanin maza da mata a makarantun Afrika 46secs
Yara maza akafi dauka a makarantun Firamare da sakadare fiye da yara mata
a akasarin kasashen Afrika.
Gibin yakairabin yara mata ake dauka kan maza a kasashe 11 ciki harda Najeriya,
da Ghana da Cote d'Ivoire,
da jumhuriyar Benin da jumhuriyar denijyradiyar Congo. Wannan kuwa yana kunshe
cikin sanarwar da majalisar
dunkin duniya ta bayar.
Sama da kasashe 18 ne suke kokari wajen cike gibin, wadanda suka haka da Masar
da Zimbabwe, da
Uganda da Habasha da Cameru dakuma Algeria. Kasashe bakwai kuma basa nuna wannan
bambancin,
yayinda Afrika ta Kudu da Lesotho kuma yaran mata ne akafi dauka cikin makarantun
fiye da yara maza.
United Nations
Matsalar ingantacen ruwan sha 14secs
Yanzu haka akwai kasashe 31 a duniya dake fuskantar matsalar karncin rwan
sha. Yazuwa shekara ta 2025
ana kyautata Zato yawan kasashen zasu karu zuwa arba'in da tawas yazuwa shekara
ta 2-50 kuma da zasuyi
fama da matsakar karancin ruwan zasu kai 55.
CGIAR
Italiya na daukar tsauraran matakai kan karya
dokokin muhalli 44secs
Yayinda take samun aiyukan cunna wuta a gandun dazuzzukan ta kowace rana
yanzu kasar Italiya ta sanya
tarar dala dubu 60 ga duk wanda aka kama da laifin cinna wuta a gandun dajin
kasar. Kana za a bada kyautar
wannan kudin ga duk wanda ya taimaka aka kamo wanda ya cinna wutar. Rahotanni
sun nuna cewar masu
cinna irin wannan wutar a Itlaiya suna janyo ta'adi mai yawa na katako da sauran
gandun dazuzzukan kasar a
duk shekara.
Kusan kowace rana sai an sami rahoton cinna wuta har sau 28 a locain bazara
a shekaru biyar da suka wuce,
yayinda filaye mai fadin kadada dubu dari biyar da arba'in ne suka kone, kamar
yadda rahoton hukumar kula
da halittu ta duniya tayi bayani.
WWF
Bunkasar alkari'u cikin hanzari a Afrika 21secs
Mutane sai kara baikin yankunan karkara suna zuwa birane a nahiyar Afrika
fiye da kowace nahiya a duniya.
Tsakanin shekarar 1995 zuwa 2025 yawan mutanen dake alkari'un Afrika zai rubanya
har sau biyu a duniya,
amma na Afrika zai rubanya sau uku a daidai wannan lokacin.
Boiling Reint 13
13 Page 14 15
Vol 11 No 10
September 1999 (Hausa) CHANGE Radio
14
Tsuntsun dake sanin locaci 59secs
Katabaji wani tsuntsu dake fadin locai? Wasu masu bincike kan halayyar tsuntsaye
a kasar Indonesia sun gano
wani abin sha'awa. Su wadan nan masu binciken da ake kira Pitta Erythrogaster,
sun gano wasu tsutsaye
masu launin ja a ciki suna iya sanin locacin dake ciki a duk twawon rana. Da
asuba tsutsayen sukan sauka kasa
su rika yin wata irin waka. Yayinda rana ta daga sai su hau kan bishiya har
sai rana ta raba tsaka. Yayinda rana
ta fara faduwa, sai tsutsayen su sauko daga rassan bishiyar har zuwa faduwar
rana. Ba anan ta tsaya ba in har
tsuntsayen sun sauka kasa batare da sun hau kan bishiya ba to ranan za'ayi ruwa.
WWF
Asarar halittu 34secs
"Babbar asarar da zata auku ba wai rashin makamashi ba ko gurguncewar tattalin
arziki, ko yaki da makaman
kare dangi ko cinyewa da yaki ba. Duk da irin wadan nan ta'adi ko asarar, yan
baya masu zuwa suna iya
farfadowa dashi. Amma babbar asara itace wanda aka fara a shekarun 1980, wanda
kuma zai dauki miliyoyi
shekaru ba a gyara ba kamar yadda wasu halittun ke bata baki daya daga doron
duniya. 'Yan baya masu zuwa
bazasu gafarta mana ba muddin muka kauda wasu halittun batare da sun sansu ba.
Edward O. Wilson
Kasar Canada na da nuhimmanci kan halittu 26secs
Canada keda kashi 10 cikin dari na dazuzzukan dake akwai a duniya, wanda
yakai kadada milyan 418, wanda
ya kai kimanin rabin fadin kasar baki daya. Wanan gandun dazuzzukan suan taimakawa
wajen kula da kashi
20 cikin dari na ingantacen ruwan sha na duniya, wanda kuma nau'o'in dabbobi
daban-daban har dibu dari da
arba'in ne ke zaune a yanki. Bugu da kari kasar itace kan gaba wajen saida albarkatun
dazuzzuka a duniya irin
su katako.
WWF 14
14 Page 15
Vol. 11 No 10
September 1999 (Hausa) CHANGE Radio
15
Kalmomin Da Akayi Amfanidasu
AAI -Kungiyar kawance bunkasa masana'an ta Afrika
ADB -Bankin raya Afrika
AIDS -Cutar Kanjamau
CGIAR -Kungiyar kwararu kan binciken aikin gona
ECA -Hukumar raya tattalin arziki na Afrika
FAO -Hukumar abinci da aikin gona ta duniya
HIV -Kwayoyin cutar kanjamau
NCF -Hukumar kula da gandun daji ta Najeriya
NGO -Kungiyoyi masu zaman kansu
OAU -Kungiyar hada kan kasashen Afrika
UN -Majalisar Dukin duniya
UNDP -Hukumar raya kasa ta duniya
UNIDO -Hukumar raya masana'antu ta duniya
UNITA -Kungiyar 'yan tawayen Angola
WWF -Asunsun kula da gandun daji da halittu 15
© 2002 Communicating for Change. All Rights Reserved
Developed by George Mbuagbaw